0
AURE KO ZAMAN GIDA ?





AURE KO ZAMAN GIDA ?


•••••PART 5•••••

…Na rogi alfarmar baba ya barni in riqa zuwa wata
yar makaranta da ake lesson anan qasa da gidanmu
baba ya amince, Kuma yace inci gaba da kare
mutuncina, Nafara zuwa lesson abubuwa da yawa
nasan sunansu amma bansan ma'anarsuba malamin
da yaga inada hazaqa sosai sai ya bani kyautar wani
littafi sunayen abubuwa da hotonsu cikin sati daya
na haddace su duka dama nasan sunayen abubuwan
kawai bansan sunayensubane sai yanzu, Ahankali
nafara iya magana da english cikin wata biyu..
Hauwa jabo ko kin gaji mu bari sai gobe nace a'ah
muci gaba kawai, Tayi murmushi taci gaba.... Ranar
nadawo daga lesson dina tun zauren gidanmu naji
wani qamshin turare mai rudarwa qamshi sosai naji
wata sassanyar murya ana wani yare bansan mi
suke cewaba a lokacin (to namifahmi hamun juri k to
hamsari man hasti uwn ham hamsari mani to
modare bachem hasti, chira mutawajji nisti ) adaidai
lokacin nabi gefensa na wuce fuskansa na kallon
yamma so baisan nashigoba na shigo tsakar gida
natararda baba fuskarsa cike da fara'a nima nayi
murmushi nace baba miya faru naganku kuna jin
dadi yace ABDUL AZEEZ ne yadawo.Waye kuma
abdul azeez baba? mijinkine, mijina? Eh Sai ban
sake cewa komaiba yayiwa su baba sayayah sosai
ina tsaye ina kallonsu, Na wuce dakina nan natarar
da kaya niqi niqi naci dana sha dana shafawa tufafi
kala kala turaruka kala kala na kira maman jamila na
nuna mata tatayani buda wasu naji dadin kayan
koba komai nasan wanda yasiyo kayan mai kudine,
Wasu kayan irin na qasar wajene bana nigeria bane
hadda waya a cikin kayana (LG G Flex) wayan ta
hadu iya haduwa sai wani envelope nagane
wasiqace naqi budawa saida maman jamila ta fita ....

Hello my wife
Sai kuma number sa daya rubuta a qasa banta6a
ganin letter irin wannan ba, Naji dadi koba komai
nasan cewa inada miji, Tun safee baba ya kirani
yace in kunna wayan da aka bani na kuwa kunna ko
minti hudu ba'ayiba kira yashigo naga ansaka AZEEZ
nidai bansan ko wayeba na dauki wayan nayi
sallama ingayamiki jabo bai amsaba saida nayi
sallama biyar ba amsa nayta danne danne har na
gane yanda ake kashewa karo na biyu ya sake kira
na dauka namma ba magana nasake kashewa karo
na na uku naqi dauka har ta qare ringing ya turo sms
(I luv d way u r talk,ur voice is agreeable ) Kwana
shida da dawowar azeez aka fara shirye shiryen
tarewana anyi min duk abubuwan da suka kamata
maman jamila ta gyarani iya qoqarinta, Aka kaini
gidan mijina in taqaitamiki labari, H jabo saida nayi
wata shida cur agidan nan bansaka Abdul azeez a
idonaba komai na gidan ya wadata ba abinda nake
nema, Duk sati za'a kawo min cefane da kudi ko
zan buqata kuma aka bani mota da driver duk inda
nakeson zuwa akaini, Ingayamiki jabo saida na
gwammace zama gida da zaman gidan aure,
Rayuwa ta sauya bana zuwa ko ina sai gida zubi
zubi tun inajin tsoro har nadaina jin tsoro nabarwa
Allah komai, Nayi magana da malaminmu mai mana
lesson akan yasamomin wanda zai riqa zuwa gida
yana mini lesson, Yasamomin wata mata tana
koyamin dan science da wasu subject na seconds
skul naba kaina wahala sosai wajen ganin na iya
karatun science Kullum ina duba internet ina daukar
lecture a internet malamar har mamakin basirana
takeyi dan kuwa har tamun hanya inje in zana waec
idan naci zata nemamin admission a university
dinsu, Sai da na zana waec naci ina zancen zuwa
kenan sai ga saqo daga mijina inje za'amun
international passport, Wata mata takaini
immigration office akamin passport aka kar6o min
ticket da visa na barin qasa..…


AURE KO XAMAN GIDA ?


PART 6


Wai ashe jabo duk zaman da nakeyi. Abdul azeez baya
nigeria gabaki daya yana iran abinshi, Ni ya zan bar
wata qasa ni kadai alhalin ban banta6a zuwa koda
airport ba, Haka nayi kuka nayi bankwana da yan
uwana dan bantabm6a tunanin zan dawoba nashiga
mota sai kaduna, Ina ganin jirgi jikina ya mutu na
tabbatarda bazanyi raiba matsawar na hau wannan
gangaramar, Wasu zafafan hawaye suka zubomin
tunda nashiga jirgi nake kuka har muka isa Lagos,
Daga lagos zamuyi fly 6:30 har aka gama shiga jirgi
ban saniba saida wata mata tamun magana sannan
nagane cewa jirginmu saura 7mnt ya tashi
tataimakamin nasamu nashiga jirgi ina shiga idon
kowa akaina har ina tuntu6e nazauna ga fitsari inaji
ina tsoron tashi, Da ya matseni haka nan na lalla6a
naje nayi amma ba ruwan tsarki naga zan batawa
kaina lokaci nasaka tissue na goge na fito, A
daddafe muka isa Beirut a Lebanon kenan, Na sake
shiga wani jirgi sai emirate dubai kenan, Nasha kallo
a dubai qasar ta burgeni sosan gaske a dubai
nasamu transit 18 hrs wllhy haka na zauna a airport
ga yunwa kamar zata kasheni na daddafa naje naci
wani abinci $50 bangane komaiba ba dadi sai dan
banzan tsami nayita amai sai zazza6i anan bacci
yayi awon gaba dani ban farkaba sai 9:12 kuma 8:30
zamuyi fly ataqaice nayi missing din fly naci kuka
har na gode Allah naje gun ma'aikatan gun namusu
bayani sukace jirgina ya wuce sai na sake sabon
bucking suka min komai da komai, Ina nan zaune
abin tausayi sai ga wata mata da mijinta zasuje iran
kuma hausawa ai kamar ansakani aljanna haka naji
nadan gaya musu yanda akayi nayi missing din fly
sukaita dariya nima saina wayance nayi dariya
amma nasan sungane ni dibgaggiyar local ce ni, Dan
kuwa kina ganina kinsan sai a slow ko a shigata,
Sun taimakamin mun isa iran nanma nayi wani
qauyanci dan kuwa anbani number akace idan na iso
airport din tehran inyi waya sai kawai nabaiwa
maman nargees kudi nace ta siyamin ticket nabisu
garinsu mashhad saida muka isa maman nargess
tasiyomin sim card nasaka nakira numbar da aka
bani, Nayi sallama aka amsa da wata sassanyar
murna mai ratsa jiki dajin muryar nagane cewa
antsorata ana tunanin na6atane kina ina yanzu,?
Airport kisamu wani mutum cikin ma'aikatan gurin
inyi magana dashi nasamu wani mutum na bashi
yagayawa. Abdul azeez cewa ina mashhad, Yaji
haushi sosai kaman in kar6i wayaya kashe nakira
ba'adauka qarshe ya kashe wayanshi natsorata
sosai naje gun wani mutumi shi ba England ba sai
surutu daga wata gasa nake (az kuzo omadid ) Ni ba
gane yarensu nakeba su kuma ba wani gwagwaran
turanci ba haka dai nasamu har ya gane me nake
nufi ya siyamin wani ticket daga mashhad zuwa
tehran inkoma inda nafito yamun komai mutanen
gasar iran akwai tsoron Allah tare dasu ga kuma
amana natashi nakoma tehran ina isa nasake
kiranshi naji wayan akashe can naji wayan yayi
ringing na dauka kina ina? Nadawo airport dinda na
sauka daga farko yayi shiru ina hello naji shiru sai
na kashe wayan ashe wai ya biyonine ni kuma
nakoma garin haka na qama zama a airport ga
qasar da wani mahaukacin sanyi wayata ta mutu
nasamu wani mutum ya nuna min masallaci nayi
sallolin da ake bina nasaka chaji sai bacci da gurin
akwai dumi ban farkaba sai asuba shima yanwa ta
tayar dani ina duba wayana naga 38 miss call. Banji
haushiba nayi sallah asuba na tashi na nemi gurin
chin abinci ina chin abinci naji ance min ke.!!…

Post a Comment

 
Top